News
’Yan Bindiga Sun Hallaka Wata Mata, Sun Sace Mutane Uku A Kano
Rahotanni daga Jihar Kano na nuni da cewa wasu ’yan bindiga dauke da makamai sun kai farmaki kauyen Yankamaye da ke cikin Karamar Hukumar Tsanyawa, inda suka kashe wata mata tare da yin garkuwa da mutane uku.
Majiyoyi daga yankin sun shaida wa Daily Nigerian cewa lamarin ya faru ne misalin 11 na dare a ranar Asabar, lokacin da mazauna garin ke shirin kwanciya.
Wani mazaunin kauyen ya ce maharan sun ajiye babur-baburansu a wajen garin sannan suka kutsa ta cikin duhu da ƙafa, domin kauce wa gano su.
A cewar majiyar, maharan sun kashe wata tsohuwa da harsashi bayan da ta roƙe su da su kyale ɗanta da suka ke ƙoƙarin tafi da shi.
“Sun harbe tsohuwar ne saboda ta nemi su bar mata ɗanta. Bayan sun kashe ta, sai suka tafi da shi,” in ji mazaunin da ya nemi a sakaya sunansa saboda tsaro.
Bayan haka, ’yan bindigar sun shiga wani gida dabam inda suka yi garkuwa da mata biyu, ciki har da surukar kansila na yankin.
Rundunar ’yan sandan Kano ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba zuwa yanzu.
Kauyen Yankamaye, wanda ke da tazarar kusan kilomita biyar daga garin Rimaye na Jihar Katsina, na daga cikin yankunan da ke fuskantar hare-haren ’yan bindiga, musamman tun bayan da wasu kauyukan Katsina suka rattaba hannu kan yarjejeniyar “sulhu” da kungiyoyin da ke kai hare-hare.
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News2 days ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News7 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
