News
Ina Nanata Cewa Babu Kisan Gilla Kan Kiristoci Ko Musulmi A Najeriya — Shugaba Tinubu
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu ya sake ƙaryata raɗe-raɗin da ke cewa ana yi wa Kiristoci kisan kare dangi a Najeriya, inda ya jaddada cewa ba bi wanda ake kaiwa hari saboda addinin sa.
Shugaban ƙasar ya bayyana cewa matsalar rashin tsaro da ke addabar Najeriya tana da alaƙa da dalilai na tarihi, tattalin arziƙi da kuma aikata laifuka, ba wai tsangwama ko kisan addini ba.
HAJJIN 2026: NAHCON Ta Sanar Da Buɗe Shafin Ɗaukar Ma’aikatan Wucin Gadi Na Kiwon Lafiya
Tinubu ya yi wannan bayani ne a ranar Juma’a a Abuja, yayin da yake buɗe babban taron shekara-shekara na ƙungiyar Nasrul-Lahi-l-Fatih Society (NASFAT).
Taron ya mayar da hankali ne kan taken: Gina juriyar al’umma a duniya mai canzawa: rawar addini da al’umma.
Shugaban ƙasar ya ƙara da cewa gwamnati na ci gaba da ɗaukar matakai domin magance matsalar tsaro da haɗa kan al’umma ba tare da nuna bambanci na addini ba.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News3 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
