News
Al’ummar Gari Sun Dakile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Al’ummar garin Rini da ke ƙauyen Bakura a Jihar Zamfara sun daƙile wani harin ’yan bindiga bayan samun bayanin isowarsu ƙauyen Yargeda da ke kusa da su.
Guda daga cikin matasan garin ya bayyana wa Aminiya cewa sun far wa ’yan ta’addan ne bayan samun labarin sun nufo garin bayan sun sace mutane a Yargeda.
Ya ce sun samu nasarar kashe gaba daya ’yan ta’addan in banda daya da ya tsere, yayin da a bangarensu wasu suka samu raunuka.
Advertisements
