News
gwamnan sokoto ya bayar da umarnin Biyan Ma’aikata Albashi Saboda Azumi
Gwamnan jihar Sokoto Ahmed Aliyu ya bayar da umarnin biyan ma’aikatan jihar albashin watan Fabarairu nan take, saboda ƙaratowar watan azumin Ramadana.
Aliyu ya sanar da hakan ne a cikin wata sanarwa ta hannun shugaban sashen yada labarai da hulɗa da jama’a na ofishin gwamnan, Abubakar Bawa a yau Alhamis.
Hukumar FRSC Ta Sallami Jami’anta 43 Daga Aiki Sakamakon Laifuffukan Da Suka Aikata
Sanarwar ta ce matakin ya shafi: “ma’aikatan Gwamnatin jiha, ƙananan hukumomi, ma’aikatan hukumar Ilimi ta ƙananan hukumomi, da kuma tsofaffin ma’aikata masu karɓar fansho a faɗin jihar”.
Bayanin ya ƙara da cewa matakin fara biyan albashin zai fara aiki ne daga ranar Juma’a 13 ga watan na Fabarairu kamar yanda BBC ta ruwaito
A ranar 18 ko 19 ga watan Fabarairun nan ne ake sa ran al’ummar Musulumi na duniya za su fara azumin watan Ramadana.
-
Opinion4 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News6 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
-
News2 days ago
Gwamna Abba Ya Ayyana Murtala Sule Garo A Matsayin Wanda Zai Yi Masa Takarar Mataimakin Gwamna A Zaɓen 2027
