Connect with us

News

Yara Huɗu Sun Nutse Ruwa A Edo

Published

on

Heavy rain causes flooding in Benue 768x576

Yara biyu sun mutu yayin da wasu biyu suka tsira bayan sun nutse a wani wurin tara ruwan ambaliya da ke titin Erediauwa, kusa da Sapele Road, a ƙaramar hukumar Ikpoba-Okha ta Jihar Edo.

Lamarin ya faru ne a ranar Lahadi, kamar yadda wata majiya ta shadawa Jaridar Punch

Advertisement

Wani shaidar gani da ido, wanda ya nemi a sakaya sunansa, ya bayyana cewa yara huɗu ne suka je wasa a kusa da wurin da gwamnatin jihar ta ware domin tara ruwan ambaliya.

Yara Biyu Sun Nutse Ruwa A Edo

Advertisement

A cewarsa, yayin da suke wasa ne suka zame suka fada cikin ruwan da ke cike da laka, lamarin da ya janyo nutsewar su.

> “Kafin agajin gaggawa ya iso, yara biyu sun riga sun rasu, yayin da aka samu nasarar ceto sauran biyun cikin mawuyacin hali,” in ji majiyar.

Advertisement

An ce an zakulo gawarwakin yaran biyu daga cikin ruwan, yayin da aka garzaya da sauran biyun zuwa wani asibiti da ke kusa domin kula da lafiyarsu.

Mai magana da yawun rundunar ‘yan sandan Rundunar ‘Yan Sandan Jihar Edo, Eno Ikoedem, ta tabbatar da faruwar lamarin.

Advertisement

Ta ce an tura jami’an ceto nan take bayan samun rahoton aukuwar lamarin, inda aka tabbatar da mutuwar yara biyun a wurin da abin ya faru.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, ba a bayyana karin bayani kan halin da sauran yaran biyu da aka ceto suke ciki ba.

Advertisement

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending