Connect with us

News

An Kama Wani Matashi Da Ke Bugar Da Marasa Lafiya Da Kayan Maye A Asibiti A Adamawa 

Published

on

Advertisements
ads

Hukumomi a jihar Adamawa sun kama wani matashi da ake zargi da shiga asibiti yana bai wa marasa lafiya kayan maye a ɓoye.

‎Rahotanni na nuna cewa ‎Ana zargin matashin da shiga asibitin koyarwa na Modibbo Adama da ke jihar Adamawa, inda yake bai wa marasa lafiya kayan maye a cikin lemu.

Gwamna Abba Ya Rungumi Akidar “Kano First” Bayan Fatali Da Tsarin Kwankwasiyya Da Ya yi; Abin Da Ya yi Siyasa ce ko Sabon Tsari? ‎ ‎ ‎

‎Matashin kan shiga asibitin ne kamar ya je duba mara lafiya, sai ya faki idon mutane ya bugar da masu jinya.

‎Bayan samun koke-koke daga cikin ma’aikatan asibitin da kuma wasu marasa lafiya, an fara sa ido a kan masu shiga da fita, wanda hakan ya kai ga kama wanda ake zargin.

‎Sai dai har yanzu babu wata sanarwa a hukumance daga jami’an tsaro ko shugabannin asibitin da ke tabbatar da cikakken bayani kan lamarin.

Advertisement

‎A halin yanzu, ana ci gaba da bincike domin gano dalilin aikata wannan abu da kuma ko akwai wasu da ke da hannu a ciki.

 

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending