News
Yan Bindiga Sun Sace Daliban Jami’ar Gwamnatin Tarayya A Nasarawa
Ɗalibai guda uku na Jami’ar Gwamnatin Tarayya ne aka ruwaito cewa ƴan bandiga sun sace su a jihar Nasarawa, duk da cewa jami’an rundunar ƴan sanda sun samu nasarar ceto guda ɗaya a yayin bincikensu, sai dai har yanzu ba a kai ga samun nasarar ceto sauran mutane biyun ba.
Mai magana da yawun rundunar ƴan sanda reshen jihar, SP Ramhan Nansel, ya tabbatar da faruwar lamarin a yau Laraba cikin wata sanarwa da ya fitar.
Rundunar ƴan sandan ta bayyana cewa lamarin sace ɗaliban ya faru ne a daren ranar Talata, a ɗakin kwanan ɗalibai da ke wani yanki a bayan gari nesa da wurin da gidajen mazauna jami’ar su ke a birnin Lafia.
Rundunar ta kuma shaida cewa ta samu kiran gaggawa ne a daren daga shugaban jami’an tsaron jami’ar, inda ya sanar mata da cewa wasu ƴan bindiga sun dirarwa gidan kwanan ɗaliban tare da sace mutane uku.
Wanda a dalilin haka nan da nan kwamishinan ƴan sandan jihar, CP Shettima Jauro Mohammed ya bayar da umarnin gaggawa na tashin tawagar jami’an rundunar don kai ɗauki.
Kakakin rundunar ƴan sandar ya bayyana cewa shirin da su ka yi ya basu damar samun nasarar ceto ɗaya daga cikin ɗaliban da aka sace, wanda kuma har zuwa yanzu suna kan ƙoƙorinsu don ceto ragowar ɗaliban.
A ƙarshe rundunar ta buƙaci mazauna yankin da su kwantar da hankalinsu tare da sanya idanu, da kuma buƙatarsu su bayar da haɗin kai ga hukumomin tsaro don taimaka musu wajen ceto sauran ɗaliban.
-
News2 days ago
Hukumar Kula Da Harkokin Shari’a Ta Tilasta Wa Alƙali Ritaya Kan Zargin Karɓar Cin Hancin Naira 250,000 A Kano
-
News3 days ago
Jigawa: Sama da Gine-gine 200 Sun Lalace Sakamakon Iska Da Ruwan Sama Mai Ƙarfi
-
News3 days ago
Wasu Fusatattun Matasa Sun Hallaka Wani Mutum Tare Da Kona Gawarsa Kan Zargin Satar Babur A Kano
