Connect with us

News

Sarkin Shanu Ya Shirya Babban Shagalin Maulidin Fiyayyen Halitta A Kano

Published

on

IMG 20260814 234617 686

Sarkin Shanu, Sarkin Maganin Gargajiya na Jihar Kano, Dr. Abubakar Yusuna, ya gayyaci al’umma zuwa shagalin Maulidin Fiyayyen Halitta, Annabi Muhammad , da za a gudanar a Kano.

A cikin sanarwar gayyatar da ya fitar, Dr. Abubakar Yusuna ya ce an shirya shagalin ne domin tunawa da haihuwar Annabi Muhammad , tare da bayyana muhimmancin koyi da kyawawan ɗabi’u da koyarwar Manzon Allah.

An Tura Kwamishinonin ’Yansanda 30 Da Jami’ai 15,000 Domin Sanya Ido A Zaɓen Osun

Sanarwar ta ce za a fara gudanar da shagalin ne daga ranar Juma’a, 1 ga watan Rabi’ul Awwal, wanda zai ci gaba har izuwa 30 ga watan Rabi’ul Awwal.

Za a gudanar da babban taron ne a Kurna Babballayi, Naira da Kwabo, a Fadar Sarkin Shaun, inda ake sa ran samun halartar ɗimbin al’umma.

Sarkin ya yi kira ga ‘yan uwa, abokan arziki da sauran al’umma da su halarci shagalin domin tunawa da rayuwar Annabi Muhammad ﷺ da kuma ƙara ƙaunar Manzon Allah a zukatan Musulmi.

Advertisement

Ya kuma yi addu’ar Allah Ya ba wa al’umma damar halartar taron cikin aminci, Ya sanya albarka a cikinsa, tare da karɓar dukkan ayyukan alheri da za a gudanar.

“Allah Ubangiji Ya ba mu ikon halarta. Amin Ya Rabbal Alamin,” in ji sanarwar.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending