Connect with us

News

Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Mutane 3 Kan Zargin Satar Taransfoma A  Neja

Published

on

Keto Electrical

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Neja ta sanar da cafke wasu mutane tara da ake zargi da hannu wajen fasa shaguna, satar kayayyaki, karɓar kayan sata da kuma satar manyan taransfoma guda biyu masu ƙarfin 1000KVA.

Rundunar ta bayyana cewa ta kwato wasu kayayyakin gyaran motoci da aka sace, waɗanda darajarsu ta kai kimanin Naira 600,000. Haka kuma, an kama wani mutum da ake zargi da safarar ɗaya daga cikin taransfoman da aka sace daga gidan wutar lantarki na Federal Housing Estate da ke yankin Tungan Shanu.

Watan Maulidi Lokaci Ne Na Yawaita Ibada Da Ayyukan Alheri – Dr Yunusa

Binciken farko da jami’an tsaro suka gudanar ya nuna cewa ana zargin an sayar da kowanne daga cikin taransfoman da aka sace kan kudi Naira 750,000.

Rundunar ’yan sandan ta ce tana ci gaba da gudanar da bincike domin gano sauran waɗanda ake zargi da hannu a lamarin, ciki har da wasu mutane biyu da har yanzu ake nema ruwa a jallo.

Ta ƙara da cewa waɗanda aka kama suna hannun jami’an tsaro domin kammala bincike kafin a gurfanar da su a gaban kotu domin fuskantar tuhuma bisa laifukan da ake zarginsu da aikatawa.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending