Connect with us

News

NAPTIP Ta Ceto Mutum 10 Da Aka Yi Fataucinsu A Kano

Published

on

Daga kabiru basiru fulatan 

 

 

 

Hukumar NAPTIP mai yaki da safarar bil’adama a Najeriya ta ceto wasu mutum goma da aka yi fataucinsu a Jihar Kano da ke Arewa maso Yammacin kasar.

 

Advertisement

Reshen Hukumar NAPTIP na Arewa maso Yamma ne ya samu nasarar ceto mutanen da ke kan hanyar zuwa Jamhuriyyar Nijar domin yin aikatau.

 

Mutum Guda Ya Mutu A Filato, Yan sanda Sun Karyata Kai Hari A Kwalejin Kimiyya

Babban jami’in NAPTIP a shiyyar Arewa maso Yamma, Barista Abdullahi Babale, ya ce an ceto mutane ne wadanda aka yi fataucinsu daga Jihohin Kogi, Delta, Kwara, Oyo, Ondo, Legas, Ogun da kuma Osun.

 

Babale ya ce hukumar tare da hadin gwiwar rundunar hadin gwiwa da ke kula da shige-da-fice a kan iyaka, sun ceto mutanen wadanda suka kunshi maza biyu da mata takwas ’yan tsakanin shekaru 9 zuwa 28.

Advertisement

 

Ya ce, a halin yanzu ana ci gaba da ba su shawarwari a wani matsuguni da hukumar ta tanada, yayin da ake kokarin mika su ga ’yan uwansu.

 

Aminiya ta ruwaito cewa a watan Maris din da ya gabata ne Hukumar NAPTIP shiyyar Arewa maso Yamma ta yi nasarar ceto wasu mutum 35 da aka yi fataucinsu a Jihar Katsina.

 

NAPTIP ta ceto mutanen ne a iyakar Kwangwalam da ke Karamar Hukumar Mai Adua a kan hanyarsu ta tsallakawa Turai.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending