Connect with us

News

Hukumar NDLEA ta gargaɗi maniyyatan Aikin Hajji

Published

on

Daga  mujahid danlami garba

 

 

 

Hukumar da ke yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya wato NDLEA ta gargaɗi mahajjata kan safarar miyagun ƙwayoyi.

 

Advertisement

Jaridar Punch a Najeriya ta ruwaito wata jami’ar hukumar Habiba Zubair a yayin da take gargaɗi a birnin Illori na Jihar Kwara a yayin da take jawabi ga mahajjatan bana.

 

Ta yi gargaɗin cewa magungunan da likitoci suka bayar da izinin sha kaɗai za a iya tafiya da su inda ta ce duk wani abu koma bayan hakan gwamnatin Saudiyya ba za ta lamunta ba.

 

Haka kuma ta yi gargaɗin cewa kada mahajaccin da ya kuskura ya karɓi kayan wani ajiya ko riƙo sakamakon za a iya ɓoye wasu abubuwan da aka haramta a cikinsu.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending