Connect with us

News

ADAMU YA BAYYANA DAMUWARSA KARARA KAN YADDA AKE FUCEWA DAGA APC

Published

on

Daga Yasir sani Abdullahi

Shugaban jam,iyyar APC na kasa Abdullahi adamu ya bayyana damuwar kan yadda ake Fucewa daga jam,iyyar Apc

Bbc Hausa ta rawaito Abdullahi Adamu ya ce ya damu matuka, kan yadda ake barin jam’iyyar.

Sanatoci bakwai ne suka sauya sheka daga APC zuwa wasu jam’iyyun, bayan sun kasa samun tikitin tsayawa takara a jam’iyyar a zaben 2023.

Sanatocin da suka fice daga APCn sun hada da tsohon gwamnan Kano Ibrahim Shekarau, da Yahaya Abdullahi daga jihar Kebbi, da Dauda Jika daga jihar Bauchi da kuma Ahmad Babba Kaita daga jihar Katsina.

Sauran sun hada da Lawal Yahaya Gamau daga Bauchi, sai kuma Francis Alimikhena daga jihar Edo.

Advertisement

Da yake magana da manema labarai bayan wata ganawar sirri da Sanatocin jam’iyyar, Mista Adamu ya ce akwai takaici irin yadda yan majalisar ke ficewa daga jam’iyyar.

” Ban damu da abinda ke faruwa a wata jam’iyya ba, damuwa ta itace abinda ke faruwa a jam’iyyata.”

” Babu Shugaba nagari da ba zai damu ba idan ya rasa mamba ko da daya ne a jam’iyyarsa, ballantana ayi maganar mamba biyu, ko uku.”, in ji Adamu.

Sai dai Shugaban APCn yace suna kan tattauna hanyar da zasu dinke wannan baraka ta ficewa daga jam’iyyar, duk da ya ce ba wani sabon abu bane

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending