Connect with us

News

Majalisar dattijai ta amince da mutanen da Buhari ke son naɗawa Ministoci

Published

on

Ahmad Lawan

Daga yasir sani Abdullah 

 

Advertisement

 

 

Advertisement

Majalisar dattijan Najeriya ta amince da sabbin ministoci bakwai da shugaba Muhammadu Buhari ya tura ma ta domin tabbatar da naɗinsu.

Yanzu-yanzu: An ga Watan Babbar Sallah Yau a Saudiyya.

Advertisement

An tabbatar da naɗin ne bayan zaman tantace su da majalisar ta yi a zamanta na wannan Larabar.

 

Advertisement

Yayinda wasu daga cikin sabbin ministocin, musamman tsohon ɗan majalisa, da aka bukaci su yi gaisuwar majalisa su wuce, wasu daga cikinsu an tsare su da tambayoyi kan abubuwan da ya shafi kasa.

 

Advertisement

Shugaba Buhari, a wata wasika da ya aikewa majalisa mai dauke da kwanan watan 15 ga watan Yuni, 2022, ya bukaci majalisar ta amince da naɗinsa.

 

Advertisement

Ya ce neman bukatar amincewa da naɗin ya yi daidai da tanadin kudin tsarin mulki sashi na 147(2) na kudin tsarin mulkin shekara ta 1999 na Tarayyar Najeriya, da aka yiwa kwaskwarima.

 

Advertisement

Ministocin da aka tabbatar da naɗin nasu sun haɗa da: Henry Ikechukwu Ikoh – daga Abia; Umana Okon Umana – daga Akwa Ibom; Ekumankama Joseph Nkama- daga Ebonyi; da Goodluck Nanah Opiah – daga Imo.

 

Advertisement

Sauran su ne Umar Ibrahim El-Yakub – daga Kano; Ademola Adewole Adegoroye – daga Ondo; da Odum Udi – daga Rivers

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending