An fara zanga-zangar neman tabbatar da mulkin dimokuradiyya a sassan ƙasar Sudan inda jama’ar ƙasar suka haɗa gangami suna neman sojoji janye daga harkokin siyasa.
An yanke hukuncin kisa ta hanyar rataya ko allurar guba kan wasu mutane a Filato
An toshe gadoji tare da katse intanet a Khartoum babban birnin ƙasar, a wani yunƙuri na hana mutane yin tattaki.
Tun a Oktoban bara, da shugabannin soji suka hamɓarar da gwamnatin riƙon ƙwarya a wani juyin mulki, ƴan Sudan ke gudanar da zanga-zanga.
Masu zanga-zanga sama da 100 aka kashe a arangama da jami’an tsaro.
Na baya-bayan nan shi ne wani matashi ɗan shekara goma sha shida da aka harbe a Khartoum a ranar Laraba.
