News
WHO ta ce korona na nan na bazuwa
Daga kabiru basiru fulatan
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya ya yi gargaɗin cewa jerin waɗanda suka kamu da cutar korona na nuna cewa har yanzu ba a kuɓuta daga annobar ba.
Gwamnatin Kano ta ƙwace lalatacciyar fulawa buhu 487
TedrosAdhanom Ghebreyesus ya ce cutar na ci gaba da yaɗuwa, don haka akwai buƙatar ƙasashe su ɗauki matakan ɗakile ta.
Ya ce, ya damu da yadda ake samun ƙaruwar kamuwa da cutar korona.
Wannan lamari yana ƙara takura tsarin kiwon lafiya dake cikin matsi, da ma su ma’aikatan lafiyar.
Yana jawabi ne a wajen taron kwamitin na WHO, wanda ya yanke hukuncin cewa har yanzu annobar na da haɗari ga lafiyar al’umma.
Kwamitin ya bayyana damuwa cewar an samu raguwar yin gwajin cutar a duk faɗin duniya, wanda hakan kuma ya shafi yadda ake sa ido a kan yaɗuwarta.
-
News6 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News3 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
-
News6 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
