News
‘Yan Nigeria da dama za su yi arziki a wannan shekara – Masanin tattalin arzikin Duniya.

Daga kabiru basiru fulatan
Fitaccen masanin tattalin arzikin Duniya, ‘Bismarck Rewane’ ya ce, ‘yan Nigeria da dama za su yi arziki a wannan shekara ta 2022.
Masanin tattalin arzikin yayi wannan hasashe ne a wajen wani taro da cibiyar kula da kasuwanci tsakanin Nigeria da Burtaniya ta shirya a Lagos.
Ya ce bangaren ICT kasuwancin da baya alaka da man fetur zai samu tagomashi mai yawa.
A cewar sa tattalin arzikin Nigeria zai bunkasa da kaso uku da digo hudu ( 3.4) a wannan shekara.
“Ba ko shakka wannan shekara za ta zamo alheri ga ‘yan Nigeria, inda al’ummar kasar kudu da arewa za su samu arziki wanda shine mafi girma da alfanu ga kasar cikin shekaru da dama da suka gabata” A cewar Bismarck Rewane.
Me za su kace kan wannan hasashe da fitaccen masanin tattalin arzikin ya yi?