Connect with us

News

‘Yan Nigeria da dama za su yi arziki a wannan shekara – Masanin tattalin arzikin Duniya.

Published

on

FB IMG 16423355639329440
Spread the love

Daga kabiru basiru fulatan

 

 

Advertisement

Fitaccen masanin tattalin arzikin Duniya, ‘Bismarck Rewane’ ya ce, ‘yan Nigeria da dama za su yi arziki a wannan shekara ta 2022.

Masanin tattalin arzikin yayi wannan hasashe ne a wajen wani taro da cibiyar kula da kasuwanci tsakanin Nigeria da Burtaniya ta shirya a Lagos.

Ya ce bangaren ICT kasuwancin da baya alaka da man fetur zai samu tagomashi mai yawa.

Advertisement

A cewar sa tattalin arzikin Nigeria zai bunkasa da kaso uku da digo hudu ( 3.4) a wannan shekara.

“Ba ko shakka wannan shekara za ta zamo alheri ga ‘yan Nigeria, inda al’ummar kasar kudu da arewa za su samu arziki wanda shine mafi girma da alfanu ga kasar cikin shekaru da dama da suka gabata” A cewar Bismarck Rewane.

Me za su kace kan wannan hasashe da fitaccen masanin tattalin arzikin ya yi?

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *