Connect with us

News

Rochas Okorocha zai yi takarar shugabancin Najeriya

Published

on

FB IMG 16432063682739072
Spread the love

Daga kabiru basiru fulatan

 

 

Tsohon Gwamnan Imo kuma ɗan Majalisar Dattawa, Sanata Rochas Okorocha, ya bayyana sha’awarsa ta tsayawa takarar shugabancin Najeriya a babban zaɓen 2023.

Advertisement

Ya bayyana hakan ne cikin wata wasiƙa da ya aika wa Shugaban Majalisar Dattawa Sanata Ahmad Lawan, inda shi kuma ya karanta ta a zaman majalisar na yau Laraba.

Okorocha wanda ɗan jam’iyyar APC ne mai mulkin Najeriya, shi ne tsohon gwamnan Jihar Imo na baya-bayan nan da ke kudu maso gabashin ƙasar.

Shi ne mutum na baya-bayan nan da ya bayyana aniyarsa ta yin takara a APC a zaɓen da za a gudanar tskanin watan Fabarairu zuwa Maris na 2023.

Advertisement

Sauran waɗanda ke fatan su gaji Shugaba Muhammadu Buhari a APC sun haɗa da jagoran jam’iyyar, Bola Ahmed Tinubu, da Gwamnan Ebonyi David Umahi, da tsohon Gwmnan Abia Sanata Orji Kalu.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *