News
Gwamnatin Najeriya Za Ta Ƙaƙaba Sharudai A Twitter, Facebook, WhatsApp, Da Sauran Kafofin Sadarwa Na Zamani
Daga Yasir sani Abdullah
Lai Mohammed ya bayyana cewa Najeriya na yin gyaran fuska ga dokar yada labarai ta kasa da kuma ka’idojin yada labarai don tabbatar da cewa duk shafukan yanar gizo da ke aiki a kasar sun cika sharuddan da aka gindaya kamar yadda aka yi da Twitter.
“Duk abin da ya shafi Twitter zai shafi duk sauran kafafen sada zumunta, walau WhatsApp, Facebook ko wani,” in ji Ministan.
Ya ce an dakatar da Twitter a Najeriya ne saboda ya zama dandalin zabi ga masu son tada zaune tsaye a kasar, da haifar da rashin hadin kai da kuma zafafa harkokin siyasa.
Ministan yada labarai da al’adu, Lai Mohammed ne ya bayyana hakan a birnin Alkahira a wata ganawa da takwaransa na Masar, Dr Amir Talaat.
-
News7 days ago
Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Kai Ziyarar Ba Zata Asibitin Kwararru Na Best Choice Dake Kano
-
Uncategorized2 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
El-Rufa’i Ya Shigar Da Ƙarar Neman Diyyar Biliyan N10 Bisa Zargin ICPC Da Nesanta Shi Da Iyalansa
