News
An kashe sarki da dogarai aka kone gawarsu a Najeriya
Daga kabiru basiru fulatan
A makon da ya gabata wasu ‘yan bindiga da ba a sansu ba sun kashe basaraken gargajiya na kauyen Agodo da ke karamar hukumar Ewekoro a jihar Ogun da ke kudu maso yammacin Najeriya, inda kuma suka kona shi tare da dogarawansa kurmus.
Rahotanni sun ce maharan sun kashe tare da kone Kabiesi Oba Odetola da dogaransa hudu, jim kadan da shigar basaraken da tawagarsa garin da kusan karfe goma sha daya na safiyar jiya Litinin 24 ga watan Janairun 2022.
Bayanai na nuna cewa wannan shi ne karo na biyu da irin wannan abin takaici ya auku a garin cikin ‘yan watannin nan.
-
News5 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Cafke Mai Safarar Makamai, Sun Kwato Harsasai 637 A Kaduna
-
News7 days ago
Jami’an NSCDC Sun Cafke Mutane Biyu Da Saniyar Da Ake Zargin Ta Sata Ce A Kano
-
News4 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
