News
Jikan Sardauna, Magajin Garin Sokoto ya rasu
Daga yasir sani abdullahi
Allah Ya yi wa Magajin Garin Sokoto, Alhaji Hassan Marafa Danbaba rasuwa a ranar Asabar a Kaduna bayan gajeruwar rashin lafiya.
Wani babban aminin marigayin ne ya tabbatar wa BBC da rasuwar Magajin Garin.
Ana sa ran za a yi janai’zar mamacin a ranar Asabar a birnin Sokoto.
Marigayin ya kasance ɗa ga Aishatu Ahmadu Bello, wadda ƴa ce ga Sardauna Ahmadu Bello.
Alhaji Hassan Marafa ne Magajin Garin Sokoto na 13 kuma an naɗa shi ne a ranar 31 ga watan Oktoban 1997
-
Uncategorized6 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News5 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News1 day ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
