Connect with us

News

Kotu ta yanke wa kurma hukunci kashi uku sakamakon sayar da wiwi a Kano

Published

on

FB IMG 1645129942855
Spread the love

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

 

Kotun Majistare mai lamba 47, ƙarƙashin Mai Shari’a Hadiza Muhammad Hassan, a jiya Litinin ta yanke wa wani kurma hukunci har kashi uku.

Advertisement

Tun da fari dai, an gurfanar da kurman ne bisa tuhumar haɗa kai da uzzurawa al’umma wajen haɗin gwiwa da wasu ɓatagari su na siyar da tabar wiwi.

Ko da jami’in kotun, Auwal Yakubu Abdullahi ya karanto masa tuhumar, nan take ya amsa laifin sa, inda hakan ya sa kotu ta yanke masa wannan hukuncin.

Hukuncin farko, an yanke masa wata 6 ko tarar naira dubu 10, sai kuma ɗaurin shekara 1 ko tarar naira dubu 30, sannan kuma sai ɗaurin wata uku ko tarar naira dubu 10.

Advertisement

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *