Connect with us

News

INEC ta sanar da ranakun da za a yi zaɓen 2023

Published

on

FB IMG 1645900061943
Spread the love

Daga kabiru basiru fulatan

 

 

Advertisement

 

Hukumar Zaɓe ta Nijeriya, INEC ta fitar da jadawalin babban zaɓe na 2023, inda da sanar da cewa za a gudanar da zaɓen shugaban ƙasa ranar Asabar 25 ga watan Fabarairun 2023.

Shugaban INEC, Farfesa Mahmud Yakubu ne ya baiyana hakan yayin wani taron manema labarai a Abuja a yau Asabar.

Advertisement

Kazalika, INEC ta sanar da cewa za a gudanar da zaɓen ƴan majalisun tarayya tare da na shugaban ƙasar.

Sannan Yakubu ya ƙara da sanar da cewa za a gudanar da zaɓen gwamnoni da na ƴan majalisun jihohi zai gudana ranar 11 ga watan Maris na 2023 ɗin.

A cewarsa, an zaɓi ranar ce saboda a tabbatar an yi aiki da sabuwar dokar zaɓe, wadda ta tanadi cewa wajibi ne a bayyana ranar zaɓen aƙalla kwana 260 kafin kaɗa ƙuri’a.

Advertisement

Ya ƙara da cewa hukumar za ta wallafa sauran tanade-tanaden dokar zaɓen “a lokacin da ya dace”.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *