News
Gwamna Sani Bello ya musanta karɓe shugabancin APC
Daga Khadija Ibrahim Muhammad
Gwamnan Jihar Naija, Abubakar Bello ya musanta karɓe shugabancin APC na riƙon ƙwarya, kamar yadda wasu kafafen yaɗa labarai su ke raɗe-raɗi.
Bello ya baiyana hakan ne ga manema labarai jim kaɗan bayan ya jagoranci ganawar da kwamitin riƙo na APC ya yi a yau Litinin a Abuja.
A cewar sa, ya gana ne da shugabannin jam’iyar na jiha kuma ya rantsar da wasu sababbin daga cikin su.
Ya ƙara da cewa ya rantsar da shugabannin jam’iya na jihohi kuma sun ɗauki rantsuwar kama aiki, sannan su ka gana a kan babban taron APC mai zuwa a ranar 26 ga watan Maris.
Da a ka tambaye shi ko a matsayin wa ya jagoranci ganawar, sai Bello ya kada baki ya ce “a matsayin shugaban riƙon ƙwarya tunda Shugaba (Buni) ya yi tafiya.”
-
News6 days ago
ICPC Ta Yi Barazanar Daurin Shekaru 7 Ga Masu Yiwa Baki Rajistar NIN A Matsayin Yan Najeriya
-
News1 day ago
Jam’iyyar ADC Ta Yi Watsi Da Cire Ta Daga Rijista, Ta Sha Alwashin Kalubalantar Hukuncin Kotu
-
News6 days ago
Hayar Jirage Hadi Sirika Ya Dakko Daga Habasha Don Damfarar Yan Najeriya Da Sunan “Nigeria Air” — Shaida
