Connect with us

News

Rikicin APC: Ni ban karɓi wata wasiƙa da ga Buni ba — Sani Bello

Published

on

Spread the love

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

 

 

 

Advertisement

Shugaban riƙo, na Kwamitin Riƙon Ƙwarya na APC, Abubakar Sani Bello, ya musanta karɓar wasiƙa da ga Shugaban kwamitin da ke cikin rikici, Gwamna Mai Mala Buni.

Daily Nigerian Hausa ta rawaito cewa rahotanni sun baiyana cewa Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ne ya bada umarnin a tsige Buni da ga shugabancin kwamitin riƙo na APC saboda zargin wargatsa shirin da a ka yi na yin babban taron jam’iyar a ranar 26 ga Maris.

Sai dai kuma wata wasika da aka ce Buni ne ya rubuta ta har ya na baiwa Gwamnan Jihar Naija umarnin ya karɓi rikon jam’iyar na wucin-gadi an gan ta tana ta yawo a kafafen sadarwa.

Sai dai kuma dan a ke ganawa da manema labarai a yau Alhamis bayan wata ganawa ta kwamitin rikon, Sani Bello ya ce bai samu wasikar ba.

Advertisement

Ya ce shi dai abin da ya sani shine jam’iyar ta aike wa da Hukumar Zaɓe Mai zaman Kanta ta Ƙasa, INEC inda ta baiyana shirinta na yin babban taron ta a ranar 26 ga watan Maris.

Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *