News
YANZU-YANZU: Muaz Magaji ya fice da ga APC
Daga maryam bashir musa
Fitaccen ɗan adawar Gwamna Abdullahi Umar Ganduje, Muaz Magaji, ya fice da ga jam’iya mai mulki ta APC a Jihar Kano.
Jaridar indaranka ta rawaito cewa Magaji na fuskantar Shari’a da Ganduje a kan laifin ƙage da yarfe a kan gwamnan, lamarin da ya sanya ya shafe kusan makonni biyu a gidan yari, kafin da ga bisani a bada belin shi.
A yau Asabar Magaji, wanda a ka fi sani da Ɗan-Sarauniya ya sanar da ficewar ta sa da ga APC a wani taƙaitaccen sako da ya wallafa a sahfinsa na facebook.
Ɗan-Sarauniya, wanda shi ne tsohon Kwamishinan Aiyuka da Gine-gine na Jihar Kano, ya ce al’umma su shaida cewa ya bar APC.
Ƙarin bayani na nan taf…..
-
Uncategorized7 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News6 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News2 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
