News
NAPTIP ta tseratar da yara 35 da za ai safarar su zuwa nahiyar turai
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Hukumar Yaƙi da Safarar Ɗan’adam, NAPTIP ta tseratar da yara 35 da za a yi safarar su zuwa nahiyar Turai a Ƙasar Nijar.
Shugaban Shiyyar Kano na hukumar, Abdullahi Babale shi ne ya baiyana haka a wata tattaunawa da Kamfanin Daillancin Labarai na Ƙasa, NAN a jiya Juma’a.
Ya ce an miƙa waɗanda a ka tseratar ɗin ga jami’an Hukumar kula da Shige da Fice ta Ƙasa, inda su kuma su ka miƙa su ga Hukumar NAPTIP a bodar Kongolam da ke Maiadua a Jihar Katsina.
Ya ce waɗanda a ka tseratar ɗin sun haɗa da maza 6 da mata 29 kuma ƴan shekaru 6 ne zuwa 42 da a ka yi safarar su da ga jihohin Ondo, Lagos, Enugu, Anambra, Oyo, Imo, Ogun, Ekiti, Edo, Osun, Kogi da Abia.
“Za a tafi da su zuwa nahiyar Turai ne ta bodar Nijar kuma mun fara bincike a kan lamarin,” in ji Babale
-
Uncategorized7 days ago
Samar Da Zaman Lafiya, Ayyukan Ci Gaba Sun Isa Shugaba Tinubu Ya Samu Wa’adi Na Biyu — Kwankwaso
-
News6 days ago
Aƙalla Mutane 40 Sun Mutu Bayan Kifewar kwale-kwale A Sokoto
-
News2 days ago
Pantami Da Yaransa Sun Fantama Min Ƙarya, Domin Babu Inda Na Ba Shi Haƙuri, Inji Hajiya Naja’atu Muhammad
