News
An kama sojan da ya kashe farar hula 7 a Borno, in ji Rundunar Sojin Ƙasa
Daga Khadija Ibrahim Muhammad
Rundunar Sojin Ƙasa a yau Juma’a ta tabbatar da kama wani soja da a ke zargin sa da kashe farar hula bakwai, da su ka haɗa da wata yarinya ƴar shekara 3 a Ƙaramar Hukumar Mafa a Jihar Borno.
Jami’in Gudanar da Binciken Sirri na Rundunar ‘Operation Hadin Kai’, Obinna Azuikpe ne ya baiyana haka a taron manema labarai kan aikace-aikacen sojoji a Arewa-maso-Gabas.
Azuikpe ya ƙara da cewa mutane 16 sun ji raunuka daban-daban a yayin harbin da sojan ya yi, wanda ya faru a ranar Talata a kasuwar Mafa.
Ya ce tuni a ka garzaya da wadanda su ka samu raunukan, inda shi kuma sojan da ya yi harbin tuni ya shiga hannun ƴan sanda.
Ya ce an kuma samun wasu lamura guda biyu inda ƴan sanda su ka hare sojoji a Maiduguri, inda ya danganta hakan da tunzuri da kuma shan kwayoyi.
-
News6 days ago
Gwamnatin Kano Ta Umarci Masu Talla Da Masu Sana’ar Jari Bola Su Bar Karkashin Gadar Tal’udu
-
News2 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News2 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
