Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun sanar da shirin ɗaukar sabbin dakarun soja 5,000 a rundunar sojan ƙasar a yaunƙurin gwamnati na yaƙar ‘yan bindigar da ke addabar yankuna daban-daban na ƙasar.
Matakin na zuwa ne yayin da Boko Haram ke ƙara tsaurara hare-hare a garuruwan da ke kudancin ƙasar masu iyaka da Najeriya da kuma ƙungiyoyin masu iƙirarin jihadi ƙawayen IS da al-Ƙa’ida a yammaci da ke da iyaka da Mali da Burkina Faso.
Akasari dai gwamnatin Nijar na ɗaukar mutum 2,000 ne duk shekara a aikin soja.
Hukumomi sun nemi matasa ‘yan shekara 18 zuwa 25 da su gabato da kansu don shiga aikin tsaron na soja da zummar kare ƙasarsu.
A cewar wata sanarwar gwamnati, za a fara ɗaukar sabbin dakarun daga watan Mayu mai zuwa.
Ficewar sojojin Faransa da ke yaƙi da masu iƙirarin jihadi a Mali ta jawo giɓi na tsaro bayan shafe shekara kusan 10.
