News
Ashe Uwa Bazata Ƙara Ganin Ɗan taba: Mahaifiyar Dadiyata ta Rigamu Gidan Gaskiya.
Daga yasir sani abdullahi
Allah yayiwa Malama Fatima Rasuwa, Mahaifiya ga Abubakar Idris (Dadiyata). Hakan na biyo bayan wani rashin lafiya mai tsanani da tayi fama dashi. Inda ta rasu ranar talata a wani asibiti dake can asibitin sojoji na 44.
Malam Muhammad wani bawan Allah ne da yake da kusanci da iyalan Dadiyata, ya shaidawa majiyar Jaridar Mikiya cewar, da asubahi aka garzaya da ita zuwa asibiti, bayan jikin nata ya yi tsanani.
Kamar yadda jaridar Daily Trust Hausa ta ruwaito, akwai wani Malam Kawali amini ga Dadiyata, ya shaida mata cewar, ƴaƴanan marigayiyar na kan hanyarsu ta komawa Kaduna, bayan samun labarin rasuwarta.
Dadiyata dai an sace shine a 1 ga watan Augusta na 2019, babu shi babu labarin sa. Sai gashi ana batun ɓatan nasa, ya rasa mahaifiyar sa.Allahu Akbar ashe Ashe Uwa Bazata Ƙara Ganin Ɗan taba.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
