Connect with us

News

Gwamna Zulum ya raba kayan abinci da kuɗaɗe ga mutum 100,000 a Borno

Published

on

Daga maryam bashir musa

 

 

 

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Zulum, ya raba kayan abinci da tsabar kuɗi ga gidaje 100,000 na marasa galihu a cikin babban birnin Maiduguri da Ƙaramar Hukumar Jere.

Da yake jawabi a wajen taron rabon a Maiduguri a jiya Talata, Zulum ya ce matakin wani ɓangare ne na rabon kayan agajin da gwamnati ke yi don rage wahalhalun da tashe-tashen hankula da annobar COVID-19 ta haifar.

Advertisement

A cewar Zulum, gwamnati ta yi bincike na tsanaki waje zaɓo waɗanda su ka ci gajiyar shirin adomin tallafa musu, musamman a wannan lokaci na azumin Ramadan.

Ya ce an kuma miƙa makamancin tallafin ga mabuƙata a sauran ƙananan hukumomin.

Zulum ya ce duk mazajen da su ka ci gajiyar tallafin za su samu buhun shinkafa kowanne, yayin da mata za su samu N10,000, da kuma kilo 5 na sukari kowannen su.

A nasa sakon fatan alheri, shugaban Ƙaramar Hukumar Maiduguri, Alhaji Bolori, ya bayyana matakin a matsayin wanda ya dace, inda ya bukaci wadanda suka ci gajiyar shirin da su rama kyautar da a ka yi musu ta hanyar amfani da lokacin Ramadan wajen yi wa jihar da kasa baki daya addu’ar zaman lafiya.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending