Wasu mahara da ake kyautata zaton masu satar mutane domin kudin fansa ne sun afkawa al’ummar Shadadi skuma sun sace mutum hudu da sanyin safiyar Laraba a karamar hukumar Kuje ta Abuja babban birnin Najeriya.
Wasu mazauna yank sun shaida wa kamfanin dillancin labarai na Najeriya NAN, cewa lamarin ya auku ne da misalin karfe 1 na dare bayan da suka rika harbin mai uwa da wabi domin tsorata mazauna yankin.
Jaridar vanguard ta ruwaito cewa wani dan uwan wandanda aka sace na cewa maharan su goma sun kutsa cikin gidan bayan balla babbar kofar shiga ciki.
Ya nemi jami’an tsaro da su taimaka wajen kwato ‘yan uwan nasa, inda ya ce dukkansu ‘yan uwan juna ne.
