News
Hamas ta kira gangami a Masallacin Kudus
Daga Muhammad Muhammad Ibrahim
Advertisements
Advertisements
Kungiyar Hamas ta Falasdinawa ta yi kira gangami a harabar Masallacin Al-Aqsa da ke gabashin birnin Kudus a ranar 5 ga watan Mayu, bayan wasu rahotannin kafafen yaɗa labaran Falasdinawa da suka ce Yahudawan masu ra’ayin riƙau na shirin ɗaga tutar Isra’ila tare da rera taken kasar a Masallacin don tunawa da Ranar ‘yancin kai na Isra’ila.
Masallacin ya kasance wurin da ake rikici na baya-bayan nan tsakanin jami’an tsaron Isra’ila da na Falasdinawa.
A wata sanarwa, ƙungiyar Hamasta ce damar da hukumomin Isra’ila suka bayar na shiga Masallacin wani mataki ne da zai haifar da tashin hankali.
Advertisements
Advertisements
