News
Ƴan bindiga sun kashe mutum 4 tare da ƙona wani gini a Ebonyi
Daga maryam bashir Musa
Al’ummar Ekpaomaka da ke Ƙaramar Hukumar Ikwo ta Ebonyi a yau Laraba sun tashi da tashin hankali yayin da wasu ƴan bindiga su ka dira garin tare da kashe mutane hudu da kuma ƙona wani gini.
Rasha ta kori jami’an diflomasiyyar Faransa 30
Steve Orogwu, shugaban Ƙaramar Hukumar Ikwo ya shaidawa manema labarai cewa ƴan bindigar sun kai hari kan Ekpaomaka, mahaifar sa, inda suka kashe yayansa da ƴaƴansa maza guda biyu da kuma wani mai gadi.
Ya ce maharan sun kuma kona gidan danginsa a harin.
“Sun kai hari gidana da daddare suka kashe babban yaya na da ’ya’yansa maza biyu; sun kashe jami’in tsaron mu tare da kona gidan mu,” inji shi.
Ya ce an ajiye gawarwakin a mutuware a Abakaliki.
Mai magana da yawun ‘yan sanda a Ebonyi, DSP Loveth Odah, ta ki cewa komai, domin ta ce ba ta yi aiki a hukumance ba.
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
