News
Fashewar tukunyar gas a Kano: Mutane 9 sun mutu 10 kuma sun jikkata –NEMA
Daga kabiru basiru fulatan
Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa, NEMA, ta tabbatar da mutuwar mutane tara, goma kuma sun jikkata sakamakon fashewar tukunyar iskar gas da ta afku a safiyar jiya Talata a titin Aba, Sabon Gari a jihar Kano.
Ko’odinetan hukumar NEMA a jihar Kano, Nuradeen Abdullahi, ya tabbatar wa manema labarai hakan yayin da yake bayar da karin haske kan fashewar tukunyar iskar gas ɗin a Kano a yammacin jiya Talata.
“Mutanen da suka mutu a fashewar iskar gas da ta afku a titin Aba da ke Sabon Gari a karamar hukumar Fagge, Kano, ya karu zuwa tara.
Kasuwar ‘yan ƙwallo: Makomar Botman, Dembele, Lewandowski, Timber, Messi, Pogba, Dennis
“An samu gawarwaki tara daga wani gini da fashewar ta shafa, kuma an ajiye su a mutuwaren asibitin ƙwararru na rundunar sojoji da ke Kano.
“Mutane goma sun samu raunuka kuma an kai su asibitoci daban-daban, inda biyu daga cikinsu an sallame su,” inji shi.
Ya kara da cewa Darakta-Janar na NEMA, Mustapha Habib ya je wajen da lamarin ya faru.
“Darakta-Janar na NEMA ne ya jagoranci tawagar ceto da kuma masu tono don tabbatar da an kwashe mutanen da suka maƙale a ƙuraguzan ginin.
“Tawagar NEMA ta ceto sun kasance a wurin da lamarin ya faru domin gudanar da bincike tare da gano illar fashewar.”
Abdullahi ya kara da cewa aikin ceton wanda aka fara da misalin karfe 10 na safe kuma aka rufe a hukumance da misalin karfe 5:15 na yamma, an yi shi ne cikin kyakkyawan tsari.
-
News4 days ago
Ban Taɓa Nadamar Adawa Da Yunƙurin Obasanjo Na Wa’adin Mulki Karo Na Uku Ba — Atiku
-
News4 days ago
Jami’an Ƴansanda Sun Ƙwato Na’urorin Solar 160 Da Darajarsu Ta Kai Kimanin Naira 59.2 A Kano
-
News2 days ago
Wasu Kansiloli Na Zargin Ciyaman Da Daukar ‘Yan Daba Domin Kai Musu Hari A Kano
