Connect with us

News

Zaɓen Fidda-gwani: Tawagar kamfe ɗin Osinbajo ta ƙaryata labarin sama wa wakilan zaɓe 7,000 masauki

Published

on

Daga yasir sani Abdullah 

 

 

 

Ofishin Tawogar Yaɗa Labarai ta Kamfe ɗin Osinbajo ta ƙaryata rahotannin da ke cewa ta yi alƙawarin kama wa wakilan zaɓe na Jam’iyar APC 7,000 ɗakuna a otal-otal a yayin zaɓen fidda-gwani na shugaban kasa na jam’iyyar.

Wacce rawa Gerrard zai iya takawa a wasansa da Man City don taimakawa Liverpool?

Advertisement

Tawagar yaɗa labarai, wacce ta bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ta fitar a jiya Alhamis a Abuja, ta buƙaci jama’a da su yi watsi da irin waɗannan rahotanni.

“Mun ga wani labari mai tada hankali cewa wata ƙungiya mai suna Osinbajo Campaign Organisation ta ce za ta samar da masaukai ga wakilan jam’iyyar APC sama da 7,000 a fadin kasar nan a lokacin zaben fidda-gwani na shugaban kasa na jam’iyyar.

“Da yake danganta wannan ikirari ga Sanata Babafemi Ojudu, mai baiwa shugaban kasa shawara na musamman a ofishin mataimakin shugaban kasa, rahoton ya yi karyar cewa Ojudu ya sanar da hakan ga wakilai a Minna yayin da yake neman su zabi Osinbajo a lokacin zaben fidda-gwani na jam’iyyar.

“Gaskiya, Ojudu bai tabba yin irin wannan ikirarin ba kuma tawogar yakin neman zaben Osinbajo ba ta tanadi wannan tsari ba.

“Ya kamata a yi watsi da wannan rahoto na cewa za a bayar da masauki da abinci kyauta,” in ji ta.

Sanarwar ta ce mataimakin shugaban kasar ya ci gaba da daukar lokaci yana tattaunawa kai tsaye da wakilan jam’iyyar APC da masu ruwa da tsaki a fadin kasar nan tare da amsa tambayoyinsu kan harkokin siyasa da mulki.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending