Sports
Man City ta lashe Premier League karo na shida
Daga Muhammad Muhammad zahraddin
Manchester City ta lashe kofin gasar Premier League ta Ingila karo na shida bayan ta farke ƙwallo biyu Aston Villa ta zira mata a filin wasa na Etihad.
Ƙungiyar da Pep Guardiola ke jagoranta ta ƙare kakar ta bana da tazarar maki ɗaya kacal tsakaninta da Liverpool, wadda ta doke Wloves 3-1 a wasan ƙarshe a yau.
Ƙwallo biyu da Ikay Gundogan ya ci da kuma wadda Rodri ya zira a cikin minti shida kacal su ne suka bai wa City nasara inda ta lashe wasan da 3-2.
Villa ta shiga gaba a wasan tun farko ta hannun Matty Cash da Philippe Coutinho.
-
News1 day ago
Shettima @60: Haƙurinsa, Biyayyarsa Sun Taimaka Wajen Ciyar Da Manufofin Shugaba Tinubu Gaba — Kwankwaso
-
News6 days ago
2027: INEC Ta Tabbatar Da Ibrahim Ali Amin Little A Matsayin Ɗan Takarar Gwamnan Kano A Jam’iyyar ADC
-
News4 days ago
KANO:’Yan Mata Uku ’Yan Gida Ɗaya Sun Mutu A Kifewar kwale-kwale A Tiga
