Connect with us

News

Peter Obi ya ja hankalin ƴan Najeriya bayan ya fice daga PDP

Published

on

Daga Muhammad Muhammad zahraddin 

 

 

 

Peter Obi na cikin manyan batutuwan da aka fi tattaunawa a Twitter a ranar Talata bayan ya fice daga talakarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP.

Gwamnonin Najeriya za su ɗaukaka ƙara kan ƙayyade kashe kuɗaɗen ƙananan hukumomi

Tsohon gwamnan na Anambra ya fice PDP yana mai bayyana cewa ba zai iya ci gaba da tafiya a jam’iyyar ba.

Advertisement

Ya ce zai ci gaba da bayar da gudunmuwarsa wajen taimakawa Najeriya magance matsalolinta.

Peter Obi ɗan kasuwa ne wanda ya shiga jam’iyyar PDP a 2017.

Ya yi takarar mataimakin shugaban ƙasa tare da Atiku Abubakar a zaɓen 2019.

Babu dai wata manufa da ta fito kawo yanzu kan daliln ficewarsa daga takarar shugaban ƙasa da kuma inda ya dosa.

Amma a kwanakin baya ƴan Najeriya musamman a Twitter sun ta alaƙanta shi da tsohon gwamnan Kano Rabiu Musa Kwankwaso kuma ɗan takarar shugaban ƙasa a jam’iyyar NNPP.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending