Politics
Na barwa Barau Jibril takarar Sanata ne saboda masalahar jam’iyya ta -inji Ganduje.
Daga mujahid danlami garba
Gwamnan Kano, Abdullahi Umar Ganduje ya ce ya hakura da takarar Sanatan Arewa ta Tsakiya domin masalahar jam’iyyar sa ta APC.
Ganduje ya bayyana haka ta cikin shirin gidan talabijin din TVC na journalists’ hangout da tsakar ranar yau Lahadi.
Yace jam’iyyar sa ta APC na amfani da tattaunawa wajen warware matsalolin dake addabar ta.
Gwamna Ganduje ya bayyana cewa Sanata Barau Jibril, tun da fari ya bayyana aniyar sata zama Gwamnan Kano, amma bisa masalaha ya janye wanda hakan tasa shi kuma ya hakura tare da barwa masa takarar Sanatan Kano ta arewa.
Advertisements
