Politics
Buhari ya bukaci tinubu ya janye takarar da yake na shugabancin kasa a jam,iyyar Apc
Daga Yasir sani Abdullahi
Jaridar the gurdiant ta rawaito cewa jigo a jam,iyyar Apc Kuma tsohon gwamnan jahar Legos bola ahmad tinubu yana ci gaba da samun matsin lamba a jam,iyyar Apc
Majiyar ta ce: “Asiwaju ransa ya baci yayin da suka isar masa da sakon shugaban kasa. A cewarsa idan shugaban kasar baya son goyan bayansa mai yasa bazai nemi su tattauna shi da shi ba sai dai a dinga kunbiya kunbiya wajen kawo masa tarnaki”.
Majiyar ta ce wannan batu ne ya harzuka Tinubu ya yi kalaman da yayi a Abeoukuta na jihar Ogun ranar Alhamis.
Haka kuma an gano cewa a tattaunawar da Buhari yayi da shugabannin jam’iyyar ya gaza gamsar da Tinubu na ya janye daga takara
Advertisements
