Connect with us

News

Najeriya ba za ta amince da digirin likitanci ba da ɗalibai suka yi a Ukraine’

Published

on

Ɗaliban Najeriya

Daga kabiru basiru fulatan 

 

 

 

Najeriya ba za ta yarda da duk wata shaidar karatu ba kan likitanci da ɗalibai suka samu daga jami’o’in Ukraine a shekarar 2022, a cewar Majalisar Likiitoci ta Najeriya ta Nigerian Medical and Dental Council (MDCN).

Shugaba Buhari nayi duk mai yiwuwa wajen magance matsalar karancin gidaje ga yan Najeriya – FHA MD

Advertisement

Majalisar wadda ke sa ido kan harkokin lafiya a Najeriya ta ce an ɗauki matakin ne saboda yaƙin da ake yi a ƙasar sakamakon hare-haren da Rasha ke kaiwa, abin da ya sa aka rufe azuzuwa na jami’o’i da manyan makarantun ƙasar.

 

“Muna sanar da jama’a cewa MDCN ba za ta yarda da shaidar karatun digiri ba kan harkokin lafiya da aka samo daga Ukraine a 2022 har sai harkokin karatu sun koma yadda aka saba,” in ji wata sanarwa da majalisar ta fitar a shafinta na Twitter.

 

Da yawa daga cikin jami’o’in na ci gaba da karatu ta intanet, matakin da MDCN ta ce ya saɓa wa manhajar koyar da likitanci.

 

Advertisement

“Domin kawar da shakku, majalisar na tabbatar da cewa duk wani horon likitanci da aka samu ta intanet ba mai karɓuwa ba ne kuma MDCN ba za ta amince da shi ba,” a cewar sanarwar.

 

Souce bbc

 

 

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending