News
Najeriya ba za ta amince da digirin likitanci ba da ɗalibai suka yi a Ukraine’
Daga kabiru basiru fulatan
Najeriya ba za ta yarda da duk wata shaidar karatu ba kan likitanci da ɗalibai suka samu daga jami’o’in Ukraine a shekarar 2022, a cewar Majalisar Likiitoci ta Najeriya ta Nigerian Medical and Dental Council (MDCN).
Shugaba Buhari nayi duk mai yiwuwa wajen magance matsalar karancin gidaje ga yan Najeriya – FHA MD
Majalisar wadda ke sa ido kan harkokin lafiya a Najeriya ta ce an ɗauki matakin ne saboda yaƙin da ake yi a ƙasar sakamakon hare-haren da Rasha ke kaiwa, abin da ya sa aka rufe azuzuwa na jami’o’i da manyan makarantun ƙasar.
“Muna sanar da jama’a cewa MDCN ba za ta yarda da shaidar karatun digiri ba kan harkokin lafiya da aka samo daga Ukraine a 2022 har sai harkokin karatu sun koma yadda aka saba,” in ji wata sanarwa da majalisar ta fitar a shafinta na Twitter.
Da yawa daga cikin jami’o’in na ci gaba da karatu ta intanet, matakin da MDCN ta ce ya saɓa wa manhajar koyar da likitanci.
“Domin kawar da shakku, majalisar na tabbatar da cewa duk wani horon likitanci da aka samu ta intanet ba mai karɓuwa ba ne kuma MDCN ba za ta amince da shi ba,” a cewar sanarwar.
Souce bbc
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
