Connect with us

Uncategorized

Hadari ya rutsa da kwambar motocin Gwamnan Jihar Benue

Published

on

Daga yasir sani Abdullah

Haduran mota da aka samu a sassan Najeriya daban-daban a karshen makon sun yi sanadiyyar mutuwar motum 30 tare da raunata wasu da kuma asarar dukiya.

Ma’aikatar lafiya ta tabbatar da ɓullar Kwalara a Kano

Advertisement

Hukumomin kasar sun danganta haduran da saba ka’idojin hanya da gudun da ya wuce kima da kuma tafiye-tafiyen dare.

Jaridar DailyTrust ta kasar ta ruwaito cewa daga cikin haduran, wasu da suka auku a tsakanin ranakun Asabar da Lahadi, sun yi sanadiyyar mutuwar mutum 18 a gadar Isara da ke jihar Ogun, kan tagwayen hanyar Lagos zuwa Badun.

Advertisement

Sannan wasu mutum 10 sun rasu a kan titin Potiskum zuwa Gombe a Jihar Yobe, yayin da wasu mutum biyu suka rasu a wani hadarin motar a kan titin Lokoja zuwa Obajana zuwa Kabba.

A hadari na hudu, wanda shi kuwa ya rutsa ne da kwambar motocin Gwamnan Jihar Benue, Samuel Ortom, a Abuja, rahotanni sun ce motoci hudu wasu tireloli biyu suka murkushe, yayin da wata motar jami’na tsaro a kwambar ta yi karo da wata motar kirar Golf, sai dai ba wanda ya rasa ransa, a hadarin.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending