Connect with us

News

Kungiyar Dillalan Man Fetur Ta Arewacin Najeriya ta Yi Barazanar Soma Yajin Aiki

Published

on

Daga yasir sani Abdullah 

 

Advertisement

 

Kungiyar masu dakon man fetur masu zaman kansu ta arewacin Najeriya ta yi barazanar shiga yajin aiki kan bayanai da hukumar kula da harkokin man fetur a kasar NMDPRA ta fitar cewa ta biya mambobin kungiyar kudadensu da suke bin gwamnati.

Advertisement

http://site1.indaranka.com.ng/?p=9642

Shugaban kungiyar, Musa Yahaya ne ya bayyana hakan yayin zantawa da manema labarai a Kano.

Advertisement

Yana mayar da martani ne kan furucin da babban jami’in hukumar kula da harkokin man fetur a kasar Farouk Ahmad ya yi cewa sun biya dillalan man fetur kudin da ya kai naira biliyan 74 a tsawon watanni bakwai da suka gabata inda kungiya reshen arewacin Najeriya suka sami naira biliyan 42.

Maikifi ya yi kira ga masu ruwa da tsaki a bangaren da su tabbabatar an biya mambobin kungiyar kudadensu daga nan zuwa karshen wata Yuli, ko kuma su tsunduma yajin aiki.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending