Connect with us

News

Shugaban mulkin soja a Sudan ya ce za su miƙa mulki ga farar hula

Published

on

Daga yasir sani Abdullah

 

 

Shugaban Sojin Sudan Janar Abdel Fattah al-Burhan ya ce sojoji za su janye su bada dama ga gwamnatin farar hula.

A jawabinsa a kafar talabijin, ya ce sojoji ba su shiga sha’anin mika mulki ga farar hula ba, kuma a shirye suke su tabbatar da an yi zaɓe.

Jama’a a Sudan na ci gaba da zaman ɗar-ɗar

Masu rajin tabbatar da dimokuradiyya sun shafe kwanaki suna zanga-zanga a sassan Sudan inda suke neman kawo ƙarshen mulkin soji.

Advertisement

A baya, Janar Burhan ya yi watsi da kudirin miƙa mulki ga farar hula.

Tun da farko hukumomi sun saki masu fafutika ɗari da arba’in waɗanda aka kama lokacin zanga-zanga a ranar 30 ga watan Yuni.

Sama da mutum 100 aka kashe tun bayan juyin mulkin da sojoji suka yi a watan Oktoba.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending