News
An rufe makarantar sakandire sakamakon mutuwar ɗalibi a Legas
Daga Khadija Abdullahi Mahmud
Ma’aikatar ilimi ta jihar Legas ta rufe makarantar framare ta Redeemers da ke garin Ogba.
Sanarwar da ma’aikatar ta fitar ta nuna cewa an dauki matakin ne biyo bayan mutuwar wani dalibi mai shekaru biyar, wanda ake zargin ya nutse a ruwa yayin wani darasin ninkaya da ake koyarwa a makarantar.
Ƴan daba sun far wa ƴan majalisar dokokin Bauchi inda su ka jikkata 6
Kwamishiniyar ilimi ta jihar Folasade Adefisayo, ta shaida wa ƴan jarida cewa makaratnar za ta ci gaba da kasancewa a rufe, har zuwa lokacin da za a kammala bincike kan ayyukanta.
A halin da ake ciki dai ƴan sanda na binciken lamarin.
Amma wani binciken farko da ofishin tabbatar da ingancin ilimi na ma’aikatar ya yi, ya nuna cewa makarantar mai suna Redeemers Nursery and Primary School ba ta kammala rajistar ta ba, don haka har yanzu ba a amince da ita ba.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
