News
Al’ummar Jihar Osun sun zaɓi wanda suke so – Buhari
Daga yasir sani Abdullah
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari, ya taya Sanata Ademola Adeleke na Jam’iyyar PDP murnar lashe zaɓen Jihar Osun da aka gudanar a ranar Asabar.
Shugaban ya bayyana haka ne a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na Facebook inda shugaban ya ce jama’ar Jihar Osun sun nuna ra’ayinsu ta hanyar jefa ƙuri’a inda ya ce dole ne a girmama abin da mutane suke so a dimokraɗiyya.
Mutumin Da Ya Auri Jikarsa A Zamfara Ya Ki Rabuwa Da Ita
Shugaban ya bayyana cewa gudanar da zaɓen da aka yi lafiya wata alama ce da ke nuna cewa an samu ci gaba da kuma haɗin kan masu ruwa da tsaki da kuma hukumar zaɓe da jami’an tsaro da jam’iyyu da yan jarida da ƙungiyoyi masu zaman kansu da masu zaɓe domin ƙara inganta harkar zabe a Najeriya.
Shugaban ya kuma ƙara jaddada aniyarsa ta gudanar da ingantaccen zaɓe a lokacin mulkinsa.
-
News1 day ago
Karuwar Ta’ammuli Da Miyagun Ƙwayoyi Tsakanin Mata Na Barazana Ga Makomar Iyali – Masana
-
Opinion5 days ago
Wakilcin Mataimakin Gwamna Garo A Taron Tsaro Na Arewacin Najeriya Abin A Yabawa Gwamna Yusuf Ne
-
News7 days ago
Wasu Da Ake Zargi ‘Yan ISWAP Ne Da Iyalansu Sun Mika Wuya Ga Dakarun Soji
