Connect with us

News

SERAP ta yi barazanar maka INEC a kotu kan rajistar katin zabe

Published

on

Daga Yasir sani abdullahi

 

 

 

 

 

Advertisement

 

Ƙungiyar SERAP mai fafutukar yaƙi da cin hanci a Najeriya ta buƙaci shugaban hukumar zabe ta INEC, Farfesa Mahmood Yakubu, ya tsawaita wa’adin rajistar katin zaɓe ko ta maka shi kotu.

 

Ƙungiyar ta yi wannan kira ne a wata wasika da mataimakin shugabanta, Kolawole Oluwadare ya fitar a jiya Asabar.

Yan bindinga sunyi garkuwa da  mutane biyu garin katsina 

Serap ta bukaci INEC ala tilas ta bai wa ‘yan Najeriya miliyan 7 da suka yi rajista a intanet damar kamala cike ka’idar mallakar katin, domin tabbatar da cewa sun yi zabe kamar yada dokar kasa ta ba su ‘yan ci.

Advertisement

 

INEC ta bayyana cewa cikin ‘yan Najeriya 10,487,972 da suka yi rajistar katin zabe ta intanet, mutum 3,444,378 ne kawai suka samu damar karban katinsu.

 

Abin da Serap ke cewa hakan na nufin kashi 32.8 cikin 100 ne kawai suka kammala matakan samun katin zabe.

 

Serap ta ce akwai bukatar ayi wa mutane uzuri la’akari da kalubalen da ‘yan Najeriya ke fuskanta a cibiyoyin karban kati a sassan Najeriya.

Advertisement

 

Ƙungiyar ta ce idan ba a ɗau matakin gyara wannan tsari ba, to ‘yan Najeriya da dama za a danne musu hakki na jefa kuri’a

 

 

BBC news

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending