Connect with us

News

Ba batun siyasa na tattauna da Bola Tinubu ba – Obasanjo

Published

on

Oba Sanjo

Daga: Muhammad Muhammad zahraddin

Tsohon shugaban Najeriya, Olusegun Obasanjo ya ce ba tattaunawar siyasa suka yi da ɗan takarar shugabanci kasa na APC ba, Bola Ahmed Tinubu.

Advertisement

Obasanjo ya gargadi magoya bayan Bola Tinubu kan yaɗa cewa ya marawa takarar Tinubu baya a ganawar sirri da suka yi a gidansa da ke Abeokuta a ranar Laraba.

Ya ce yaɗa irin wadannan labarai marasa tushe na lahani ga ‘yan siyasa irinsu Tinubu.

Advertisement

A wata sanarwa da maitaimaka ma sa na musamman ya fitar, kehinde Akinyemi, na ambato Obasanjo na cewa ganawarsa da Tinubu ta ‘yan uwantaka ce ba siyasa ba.

Wannan na zuwa ne bayan kakakin majalisar wakilai, Femi Gbajabiamila a wani taro na APC a Lagos ya na mai cewa ganawar Obasanjo da Tinubu alamar nasara ce garesu a zaben 2023.

Advertisement

Tsohon shugaba Obasanjo dai ya sake jadada cewa shi uba ne ga duk ‘yan Najeriya da matasa da ke cikin matsi.

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending