Connect with us

News

Sojojin Najeriya sun kaddamar da bincike kan kisan Goni Aisami

Published

on

Goni Aisami

Daga Muhammad Muhammad zahraddin

Rundunar sojojin Najeriya ta ce ta kaddamar da bincike kan kisan da aka yi wa fitaccen malamin addinin Musuluncin nan na jihar Yobe, Sheikh Goni Aisami.

Advertisement

Mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar ta biyu ta Operation Hadin Kai, Kennedy Anyawu, ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi a Damaturu.

Rundunar ta ce tuni ta kama sojoji biyu, kofur John Gabriel da kofur Adamu Gideon a kan batun kisan malamin.

Advertisement

Rundunar da hadin gwiwar rundunar ‘yan sandan jihar Yobe ne za su gudanar da bincike don gano wadanda suka aikata wannan aika-aika.

Kazalika rundunar ta kuma kafa wani kwamiti da zai bankado yadda lamarin ya auku.

Advertisement

Idan aka kammala bincike aka gano wadanda suka aikata kisan to lallai za su fuskanci hukunci da ya kamata in ji rundunar.

Kisan malamin ɗan Jihar Yobe ya ja hankalin ‘yan ƙasar musamman ma’abota shafukan zumunta.

Advertisement

A ranar Juma’ar da ta wuce ne aka kashe malamin a lokacin da yake tuƙa motarsa a kan hanyar zuwa Gashua daga Nguru.

Advertisement
Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending