Connect with us

News

An kama injiniyan ginin da tanki ya faɗo wa mutane 2 suka mutu a Legas

Published

on

 

 

Daga: Yasir sani abdullahi

 

 

 

Advertisement

 

 

 

 

 

Ƴan sanda a jihar Legas sun kama injiniyan da ya yi aikin ginin da wani tankin ruwa ya fado ya kashe mutane biyu a ranar Lahadi.

Advertisement

Kakakin rundunar ‘yan sanda a jihar, SP Benjamin Hundeyin ne ya tabbatar da cafke injiniyan a yau Talata.

Ya shawarci jama’a da su guji amfani da injiniyoyi na boge .

“Kada ku yi amfani da injiniyoyi da basu cancanta ba.

“Injiniya yana hannunmu. Ana ci gaba da gudanar da bincike.’’ Mista Hundeyin ya ce.

Ibrahim Farinloye, Ko’odinetan shiyyar Kudu maso Yamma a Hukumar Ba da Agajin Gaggawa ta Kasa, NEMA, a jiya Litinin din da ta gabata ya bayyana cewa wani tankin ruwa da ke saman wani gini ya fado tare da kashe mutane biyu a Ladi Lak da ke yankin Bariga a Legas.

 

Advertisement

Daily Nigerian

Advertisements
Advertisement
Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Trending